Wasanni
Al Ahly ta Masar na cikin tsaka mai wuya
Kungiyar kwallon kafa ta Al Ahly da ke Masar ta shiga tsaka mai wuya a rukuninta na A a gasar cin kofin zakarun Afrika bayan da ta sha kashi ci 2-1 a gida a hannun ASEC Mimosas a fafatawar da suka yi a filin wasa na Borg El Arab a jiya Talata.
Wallafawa ranar:
Talla
A karo na biyu kenan da kungiyar ke shan kashi a rukunin bayan da Zesco United ta casa ta a waje a wasansu na farko da suka yi a farkon wannan watan.
Wannan dai ya haifar da koma baya ga kungiyar wadda ke neman daukan kofin gasar a karo na takwas.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu