Isa ga babban shafi
Wasanni

CAF ta yi watsi da bukatar Musa Bility na takarar FIFA

Hukumar kwallon kafar nahiyar Africa CAF ta ki amince ta goyawa Musa Bility na liberia baya, domin tsayawa takarar maye gurbin Sepp Blatter shugaban hukumar kwallon kafa ta Duniya wato FIFA

Shugaban Hukumar Kwallon kafar nahiyar Africa CAF Issa Hayatou.
Shugaban Hukumar Kwallon kafar nahiyar Africa CAF Issa Hayatou. AFP PHOTO / FADEL SENNA
Talla

Bayan gudanar da wani tattaunawa da suka yi shugabannin hukumar ta CAF sun nuna cewa, ba za su marawa Musa Bilitiny baya ba kamar yadda ya bukata, daga wajen hukumar sai dai tana masa fatan alheri a harkokin sa na kasuwanci.

Tun dai a cikin watan Yuni da ya gabata ne  Bility wanda shine shugaban hukumar kwallon kafa Liberia tun shekarar 2010 kawo yanzu, ya nuna sha’awarsa na tsayawa wannan takara.

Yanzu dai haka Zico fitaccen dan wasan Brazil da ya yi tashe a baya da kuma attajirin kasar Korea ta kudu Chung Mong-Joon sune suka nuna sha'awarsu na karawa a neman wannan kujera.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.