Batun Qatar na da nasaba da wariyar launin fata- Blatter
Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, Sepp Blatter ya mayar da martani kan wadanda ke zargin hukumar da karbar cin hanci wajen bayar da daukar nauyin gasar cin kofin duniya da za a yi a Qatar a shekarar 2022, inda ya ce mutanen dake wannan zargi, so kawai suke su wargaza hukumar ta FIFA.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Dan shekaru 78, Blatter ya yi wadannan kalamai ne yayin wata ganawa da ya yi da hukumomin kwallon kafa na nahiyar Asiya da Afrika, yayin da ake shirin bude taron wakilan hukumar ta FIFA a karo 64 a yau Talata.
Ya kuma kara da cewa zargin da ake yi kan badakalar ta Qatar na da nasaba da wariyar launin fata idan aka kalli lamarin ta wata fuska.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu