Isa ga babban shafi

Manoma a Faransa sun yi barazanar kara azama a zanga-zangar da suke yi

Kungiyar manoma mafi girma a kasar Faransa na shirin gudanar da gagarumin zanga-zangar gama gari a cikin makwanni masu zuwa don nuna rashin amincewa da harajin da gwamnatin kasar ta dora a kan man katafilar noma, da kuma yadda ta bari suke shan wahala wajen gogayya da kayayyaki masu araha daga kasashen waje.

Manoma a  daa ke zanga-zanga a birnin Toulouse sun haddasa cinkoson motoci.
Manoma a daa ke zanga-zanga a birnin Toulouse sun haddasa cinkoson motoci. AFP - ED JONES
Talla

Kakakin kungiyar ne ya bayyana haka a cikin karshen makon da ya wuce, lamarin da ke fadada zanga-zangar manoma a kudu maso yammacin kasar, wadanda suka datse babbar titi, tare da zuba taki a gine-ginen gwamnati.

 

Daruruwan manoma da katafilar noma ne ke zanga-zanga a birnin Toulouse dake kudu maso yammacin kasar Faransa, lamarin da ya haddasa cinkoson motoci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.