Isa ga babban shafi

Masu zanga-zanga sun kona gidan wani magajin gari a Paris

A Lahadi, Fira minister Faransa, Élisabeth Borne ta yi tir da harin da masu zaga-zanga suka kai gidan wani magajin gari na wani birni a kewaye birnin Paris, inda  har suka banka wa gidan wuta, harin da ta bayyana a matsayin abin takaici.

Zanga -zanga ta barke a Faransa saboda kashe wani matashi da wan dan sanda ya yi.
Zanga -zanga ta barke a Faransa saboda kashe wani matashi da wan dan sanda ya yi. © Pascal Rossignol / Reuters
Talla

Borne ta yi kira da a hukunta wadanda suka aikata wannan aika aika a gidan magajin garin L’Hay-Les Roses, Vincent Jeanburn.

Jeanburn ya ce mai dakinsa da ‘yayansa biyu, masu shekaru 7 da 5 sun samu rauni a yayin da suke tserewa daga wannan farmaki da masu zanga zanga suka kai musu.

Da take ziyarar birnin na L’Haÿ-les-Roses a ranar Lahadi, Fira ministar  ta ce  ba zai yiwu a kyale wadanda suka aikata wannan mummunan aiki ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.