Isa ga babban shafi

Adadin mutanen da aka kama sanadiyar tarzomar Faransa ya haura dubu biyu

Sama da mutane dubu 2 ne aka kama a Faransa, tun bayan tarzomar da ta biyo bayan kisan da 'yan sanda suka yi wa matashi Nahel, kamar yadda ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar ta sanar a yau Lahadi.

Jami'an 'yan sandan Faransa.
Jami'an 'yan sandan Faransa. © AP / Christophe Ena
Talla

Daren jiya Asabar wanda kuma shine na biyar a jerin dararen da aka faro zanga-zangar kisan matashin, hukumomin Faransa sun tabbatar da kama mutane 719.

Ma’aikatar kulada harkokin cikin gida ta kasar, ta ce ana kuma samun raguwar tarzomar da aka faro tun a ranar Talatar da ta gabata.

Ministan kulada harkokin cikin gida na Faransa Gerald Darmanin, a jiya Asabar ya sanar da shirin tura jami’an ‘yan sanda dubu 45 sassan kasar don kwantar da tarzomar a daren na Asabar.

A jiya ne dai aka binne matashin, inda ‘yan uwa da abokan arziki ke cike da alhinin rashinsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.