Mahammed Sala na Liverpool, ya ce sakaci ne ya hana su samun gurbi a gasar zakarun turai
Dan wasan gaban fagen kungiyar kwallon kafar Liverpool Mohamed Salah, ya bayyana cewa, hankalinsa ya yi matukar tashi kan rasa gurbin buga gasar cin kofin Zakarun Turai a kaka mai zuwa. inda ya kara da cewa, babu wata magiya ko neman afuwa da za a yi a kan wannan rashin nasara.
Wallafawa ranar:
Salah ya yi wannan sanarwa ne a shafin yada labaran yanar gizo, jim kadan bayaan rashin nasarar da Liverpool ta cimma a bayan kungiyoyi hudun farko dake kan gaba, sakamakon nasarar da Manchester United ta yi kan Chelsea.
Liverpool da ta kare ne a matsayi na 5, za ta halarci gasar cin kofin kwallon kafar 'Europa League a kaka mai zuwa.
Dan kasar Masar mahamed Sala, mai shekaru 30 a duniya ya bayyana cewa, sun kada magoya bayansu, haka kuma su da kansu.
Liverpool dai ta yi nasarar lashe wasanni bakwai daga cikin takwas da ta buga, a kokarinta na kaiwa ga matsayin na hudu, sai dai ba ta samu damar cimma wannan buri nata, bayan buga wadannan jerin wasanni da ta yi .
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu