Isa ga babban shafi

'Yan sandan Turkiya sun cafke mutane fiye da 100 bisa zarginsu da ta'addanci

Jami’an tsaron Turkiyya sun kama mutane 110 bisa zarginsu da alaka da ta'addanci, makwanni uku kacal kafin kada kuri'a a zaben ranar 14 ga watan Mayu, wanda da ake sa ran zai tsawaita wa'adin mulkin shugaba Recep Tayyip Erdogan da tsawon shekaru goma.

'Yan sandan Turkiya cikin shirin ko ta kwana.
'Yan sandan Turkiya cikin shirin ko ta kwana. REUTERS - MURAD SEZER
Talla

Bayanai sun ce jami’an tsaron sun kai samame ne a sassan larduna 21, cikinsu har da yankin Diyarbakir da ke kudu maso gabashin kasar ta Turkiya, wanda kuma mafi rinjayen mazaunansa Kurdawa ne.

Sai dai kungiyar lauyoyin yankin Diyarbakir ta ce adadin mutanen da ake tsare da su zai kai 150, cikinsu kuma  har da lauyoyi 20, ‘yan jarida biyar, ‘yan wasa uku da kuma dan siyasa daya.

Kafar yada labaran kasar ta TRT ta rawaito cewa, 'yan sanda sun cafke mutanen fiye da 100 ne, bisa zarginsu da  tallafa wa haramtacciyar kungiyar PKK.

Kamen ya kuma shafi wasu da ake zargi da aika kudi zuwa ga kungiyar ta PKK, ta hannun wasu kananan hukumomin da ke karkashin ikon babbar jam'iyyar adawa ta Turkiya HDP.

PKK wadda Amurka da Tarayyar Turai da Turkiyan suka sanya ta cikin kungiyoyin ‘yan ta’adda, ta shafe gwamman shekaru tana fafatawada sojojin gwamnati da  zummar neman 'yancin cin gashin kai ga tsirarun Kurdawa.

Shugaban Turkiya Recep Tayyib Erdogan dai ya sha zargin cewa akwai alaka tsakanin jam'iyyar adawa ta  HDP da PKK, zargin da jam'iyyar ta musanta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.