An yi arangama tsakanin 'yan sanda da masu adawa da kulle a Australia
Dubban mutane ne suka yi tattaki a birni na biyu mafi girma a Australia a wata zanga zangar adawa da dokar kulle a yau Asabar, lamarin da ya janyo arangama da ‘yan sanda a birnin Sydney.
Wallafawa ranar:
An kama gwamman mutane bayan zanga-zangar da suka gudanar ba bisa ka’ida ba ya saba dokokin kiyaye lafiya a birnin Sydney, a yayin da aka yi ta dauki-ba-dadi da ‘yan sanda yayin gangamin da aka shafe sa’o’i ana yi.
An yi ta jifan jami’an tsaro da tukwanen furanni da kwalaben ruwa a yayin da masu adawa da dokar zama a gida don dakile yaduwar annobar Covid-19 da ta shafe watanni tana aiki a birnin suka bazama tituna.
Zalika, dubban masu zanga- zanga sun taru a tituna da daman a birnin Melbourne bayan wani taro a wajen ginin majalisar dokokin jihar a tsakar ranar wannan Asabar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu