Fafaroma Francis ya jaddada kiran zaman lafiya a Myanmar
Fafaroma Francis ya gudanar da sujada ta musamman don tunawa kasar Myanmar a Lahadin nan, inda ya jaddada kiraye-kirayen da yake na kawo karshen tashin hankali a kasar da ake ta zub da jini tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi.
Wallafawa ranar:
Sujadar Mass din da aka gudanar a majami’ar Saint Peter Basilica ta birnin Vatican na zuwa ne bayan kiraye kirayen zaman lafiya da shi Fafaroma Francis, wanda ya ziyarci Myanmar a watan Nuwamban 2017 ya shafe watanni yana yi.
Wata limamiyar ‘yar asaklin Myanmar ce ta gabatar da karatun farko cikin harshen Burma a sujadar da ta samu halartar limamai mata da maza kimanin 200.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu