Zan doke Joshua tun a zagaye na biyu - Fury
Tyson Fury ya yi ikirarin cewa zai doke zakaran damben Boxing ajin nauyi Anthony Joshua tun a zagaye na biyu a fafatawar da suke shirin yi, saboda a cewarsa yanayin kwari da yake ji kwanan nan.
Wallafawa ranar:
Fury mai rike da kambin WBC ya ce biyo bayan fafatawa biyu da Joshua ya yi da suka bashi nasara a kan Andy Ruiz Junior a watan Disambar 2019 da kuma zagaye har na tara kafin doke Kubrat Pulev a watan da ya gabata, yace Joshua bazai kai labari a kansa ba.
Dama dai fafatawar da ake jira kenan, tun bayan nasarar da Anthony Joshua ya samu a karawar karshe da yayi da Kubrat Pulev a watan Disemba.
Yanzu haka Anthony Joshua shi ke rike da kambin duniya ajin nauyi na damben zamani, bayan doke Kubrat Pulev, a karan-batta da zaratan ‘yan damben Boxing din sukayi a birnin London.
Joshua na Birtaniya amma dan asalin Najeriya ya kare kambunsa na IBF da WBA da WBO a filin wasa na Wembley kuma a gaban ‘yan kallo kimanin dubu 1 da aka takaita yawansu saboda annobar coronavirus.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu