Joshua zai kare kambinsa a karawarsa da Pulev
A wannan Asabar ake karan-batta tsakanin zaratan ‘yan damben Boxing wato Anthony Joshua da Kubrat Pulev a birnin London.
Wallafawa ranar:
Sau biyu aka dage fafatawa tsakanin jaruman guda biyu saboda raunin da Pulev na Bulgaria ya samu a kafadarsa da kuma annobar coronavirus.
Yanzu haka Joshua na Birtaniya amma dan asalin Najeriya zai kare kambunsa na IBF da WBA da WBO a ranar Asabar a filin wasa na Wembley kuma a gaban ‘yan kallo kimanin dubu 100 da aka takaita yawansu saboda annobar coronavirus.
Raban da Joshua ya fafata da wani dan dambe, tun lokacin da ya doke Andy Ruiz a Saudiya watanni 12 da suka gabata, wasan da ya ba shi damar karbe kambun WBA da WBO da IBF.
Dan wasan ya ce a shirye yake ya sha dukkanin naushe-naushe har matakin karshe na fafatawarsa da Pulev.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu