Akwai sabani tsakanina da shugaban Faransa - Merkel
A karon farko shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta tabbatar da cewa akwai sabanin ra’ayi tsakaninta da shugaban Faransa Emmanuel Macron.
Wallafawa ranar:
Merkel ta bayyana haka ne yayin zantawa da jaridar Süddeutsche Zeitung ta kasar Jamus da aka wallafa a ranar Larabar da ta gabata.
A ‘yan watanin baya bayan nan dai shugabanin biyu sun fuskanci rashin fahimtar juna, kan batutuwa da dama, musamman dangane da soke cinikin saidawa Saudiya makamai da Jamus ta yi, biyo bayan kashe dan jarida Jamal Khashoggi, da ake zargin dan sarkin kasar Muhammad bin Salman da hannu a ciki, da kuma makomar nahiyar turai, sai kuma batun ficewar Britaniya daga cikin kungiyar kasashen Turai na karin lokacin da aka yi mata
Sai dai shugabar gwamnatin ta Jamus ta bayyana a cewa an samu ci gaba mai yawa sakamakon huldar diflomasiyar da ke tsakanin kasarta ta Jamus da Faransa, musaman kan sha’anin da ya shafi tsaro.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu