Isa ga babban shafi
Jamus

Merkel na tattaunawa da 'yan adawar siyasa

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta fara tattaunawa da shugaban jam’iyyar adawa ta Social Democrats SDP, Martin Schulz, domin kawo karshen halin rashin tabbas da siyasar kasar ta Jamus ta tsinci kanta.

Shugabar Jamus, Angela Merkel.
Shugabar Jamus, Angela Merkel. REUTERS/Eric Vidal
Talla

Bayan zaben Jamus na watan Satumba da Merkel ta gaza samun rinjayen da take bukata na kafa gwamnati, jam'iyyar adawa ta SPD ta ce ba za ta sabunta kawance kafa gwamnati da Merkel din ba.

Sai dai bayan rushewar kokarin Angela Merkel na samun hadin kan sauran jam’iyyun adawa na FDP da Greens a farkon wannan watan, jam’iyyar SPD ta Martin Schulz ta fuskanci karin matsin lamba daga shugabanni dama sauran ‘yan kasar ta Jamus kan ta amince da sabunta kawancenta da gwamnatin Merkel.

Angela Merkel ita ce shugabar jam’iyya mai mulkin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.