Isa ga babban shafi
Turkiya

Majalisar Turai ta amince a jingine bukatar Turkiya

Majalisar dokokin Tarayyar Turai, ta bukaci a kawo karshen duk wata tattaunawa da Turkiya dangane da yunkurin kasar na zama mamba a kungiyar, sakamakon adawa da majalisar ke yi da gyaran kundin tsarin mulkin kasar da ya kara karfin iko ga shugaba Racep Tayyip Erdagon.

Shugaban Turkiya Tayyip Erdogan
Shugaban Turkiya Tayyip Erdogan REUTERS
Talla

A kuri’ar da aka jefa a jiya Alhamis ‘yan Majalisa 477 ne suka goyi bayan matakin katse tattaunawar, yayin 64 suka nuna adawarsu.

Kudurin dai ya bukaci a dakatar da duk wata tattaunawa da Turkiya idan har kasar ta tabbatar da kundin tsarin mulkin da aka yi wa kwaskwarima.

A watan Mayu, shugaba Erdogan ya ce ba zai koma yana bara ba, yanzu ya rage ga Tarayyar Turai ya yanke shawara akan bukatar kasarsa na zama mamba a kungiyar.

Daga cikin sabbin dokokin da kasashen Turai ke adawa da su a kundin tsarin mulkin sun hada batun dawo da hukuncin kisa a Turkiya inda kasashen ke son a zauna domin fahimtar juna kafin karshen shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.