Faransa ta kafa rundunar yakar ta’addanci
Gwamnatin Faransa ta sanar da kafa wata runduna ta musamman da za ta kunshi zarata daga hukumomin tsaro da kuma tara bayanan sirrin domin yaki da ayyukan ta’addanci a kasar.
Wallafawa ranar:
Daukar matakin dai ya biyo bayan karuwar hare-haren ta’addanci a kasar, cikin har da harin da wani mutum ya kai wa ‘yan sanda da guduma a jiya laraba, yayin da makwabciyar kasar Birtaniya ke ci gaba da juyayin harin da ya kashe mutane 7 a London
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce wannan barazana ce da ke kara tabbatar da cewa dole ne a kara daura damara a yaki da ayyukan ta’addanci.
Faransawa uku suka mutu a harin London da wasu guda 7 cikin wadanda suka jikkata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu