Isa ga babban shafi
Faransa

Le Pen ta kwafi jawabin Fillon

An zargi ‘Yar takarar shugabancin Faransa Marine Le Pen da satar jawabin Francois Fillon na Jam’iyyar Republican da ya sha kaye a zagaye na farko a wani jawabin da ta gabatar a ranar Litinin a Paris.

'Yar takarar Jam'iyyar FN Marine Le Pen a Faransa
'Yar takarar Jam'iyyar FN Marine Le Pen a Faransa REUTERS/Charles Platiau
Talla

Le Pen ta gabatar da jawabinta kamar na Fillon ba tare da sauya kalma ba.

A ranar 15 ga watan Afrilu ne, Fillon ya bayyana a cikin jawabin da ya gabatar a Puy-en-Velay cewa Fransa nada iyaka ta tsaunukan da suka hada ta da kasar Italiya ‘yan uwa, da wani gefen kasar Sifaniya kai har zuwa Turai ta tsakiya da balkan da kuma yammacin Turai.

Amma Kwanaki 15 bayan gabatar da wannan jawabi, na Fillon, a lokacin da ta ke jawabi a gaban magoya bayanta a Villepinte a Seine-Saint-Denis, Le Pen, a kokarinta na son birge magoya bayanta ta maimaita kalmomin da Fillon ya yi amfani da su a jawabinta.

A ranar Lahadi ne Le Pen za ta fafata da Emmanuel Macron a zaben shugaban kasa zagaye na biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.