Isa ga babban shafi
Faransa

Nathalie Arthaud ‘Yar takarar Zaben Faransa na 2017

Nathalie Arthaud mai gwagwarmayar kare hakkin ‘yan kwadago, na daya daga cikin ‘yan takara 11 da za su kara da juna a zagayen farko na zaben shugabancin Faransa na 2017 da za a gudanar a ranar 23 ga wannan wata na Afrilu.

Nathalie Arthaud, 'Yar takarar zaben shugaban kasa a Faransa
Nathalie Arthaud, 'Yar takarar zaben shugaban kasa a Faransa AFP/Joël Saget
Talla

Tarihin Nathalie Arthaud
An haifi Nathalie Arthaud a 1970 a jihar Drôme da ke kudu maso gabashin kasar Faransa, tun tana ‘yar shekaru 18 a duniya ta tsunduma gwagwarmayar kungiyoyin kwadago.

Ta yi karatunta ne a fannin shi’anin tattalin ariziki da dangoginsa, kafin ta yi aikin koyarwa a ungunannin marasa galihu da ke birnin Lyon.

Tun a 2002, Nathalie Arthaud ta ke tsayawa takara a zabubbukan majalisun kananan hukumomi, majalisar dokoki, manyan yankunan Faransa da na kasashen turai.

Ta zama ‘Yar majalisar karamar hukumar Vaulx-en-Velin da ke jihar Lyon kafin ta zama mai magana da yawun Arlette Laguiller matar da ta taba tsayawa takarar nemen shugabancin Faransa a 2007 a yayin da a 2008 ta zama kakakin ‘yan gwagwarmayar kungiyoyin kwadagon kasar.

A 2012 ta taba tsayawa takarar neman zama ‘yar majalisar dokoki inda ta sha kaye a mazabarta ta da’ira ta 6 da ke unguwar Seine-Saint-Denis a birnin Paris.

Wannan duk bai sanyaya guiwar wannan gwarzuwar ‘yar siyasa ba, inda a 2015 ta sake yin takara a zaben yankunan Faransa da suka hada da na Ile de France ba tare da samun nasara ba.

A ranar 12 ga Maris na 2016 ne, gungun masu gwagwarmayar neman kare hakkin ‘yan kwadago ya tabbatar da ita a matsayin ‘yar takarar da za ta wakilce su a zaben shugabancin kasar na 2017.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.