Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa na shirin tsawaita wa’adin dokar ta baci

Firaiyi ministan Faransa Manuel Valls ya ce akwai yiwuwar kara tsawaita wa’adin dokar ta bacci da aka sanya a kasar bayan hare-haren ta’addancin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane dari daya da talatin a bara.

Shugaba Obama da shugaba Hollande da magajiyar garin Paris Hidalgo a bukukuwan tuna harin Paris
Shugaba Obama da shugaba Hollande da magajiyar garin Paris Hidalgo a bukukuwan tuna harin Paris REUTERS/Philippe Wojazer
Talla

Mista Valls ya ce akwai bukatar ci gaba da aiki da dokar ganin Faransa na shirin gudanar da babban zaben shugaban kasa al’amarin dake bukatar tsaro don kare lafiyar al’umma.

A ranar sha uku ga watan Nuwambar shekarar 2015 aka kai hare-haren ta’addancin da suka yi sanadiyyar mutuwar mutane 130 a Bataclan da kuma wasu filayen wasanni da ke birnin Paris.

Ana dai ci gaba da taron bukukuwan cika shekara guda da kai hare-haren birnin Paris da ya matukar girgiza al’ummar kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.