Muhawarar Jam'iyyar Republican na Faransa kan zaben 2017
Masu neman shugabancin Faransa a Jam’iyyar Republican mai adawa za su gudanar da wata babbar muhawara a yau Alhamis domin tsayar da daya daga cikinsu a matsayin dan takarar Jam’iyyar a zaben da za a gudanar a 2017.
Wallafawa ranar:
‘Yan takarar sun hada da tsohon shugaban kasa Nicolas Sarkozy da tsohon Firaminista Alain Juppe da sauran ‘Yan takara 5 da suka hada da Francois Fillon tsohon minister a gwamnatin Jacques Chirac.
Gwamnatin Francois Hollande, wanda ke fuskantar kalubali musamman a fanin tsaro, har yanzu bai bayyanan matsayinsa na sake tsayawa takarar ba.
Sai dai ga dukkan alamu jam’iyyar Hollande ta Socialist na fuskantar koma baya a kuri’un jin ra’ayin ‘yan kasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu