Isa ga babban shafi
Venezuela

'Yan adawa sun sake kaddamar da zanga zanga a Venezuela

Yan adawa a kasar Venezuela sun sake kaddamar da sabuwar zanga zanga domin tilastawa shugaban kasar Nicolas maduro bawa jama'ar kasar damar kada kuri’ar sauke shi daga mukaminsa. 

Sabuwar zanga zangar adawa da Shugaban Venezuela Nicolas Maduro
Sabuwar zanga zangar adawa da Shugaban Venezuela Nicolas Maduro REUTERS/Christian Veron
Talla

Sabuwar zanga zangar ta zo sati guda bayan gudanar da makamanciyarta a babban birnin kasar Caracas.

Magoya bayan gamayyar jam’iyyun adawa na MUD sun yi ikirarin cewa dole Maduro ya sauka da mukaminsa, saboda gazawarsa karara wajen magance tabarbarewar tattalin arzikin kasar.

Venezuela na fama da karancin abinci da magunguna a asibitoci.

Har yanzu dai ‘yan adawa a kasar suna cigaba da kokawa bisa yadda suka ce jami’an tsaro suna kame magoya bayansu, musamman a zanga zangar da ta gudana a ranar Alhamis din da ta gabata.

 

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.