Isa ga babban shafi
AFGHANISTAN

An farfado da tattaunawar sulhu da ‘yan Taliban

Pakistan na daukar nauyin wani taro domin farfado da tattaunawar zaman lafiya tsakanin ‘yan Taliban da kuma gwamnatin Afghanistan

Sojin kawance na kungiyar NATO a birnin Kabul na kasar Afghanistan
Sojin kawance na kungiyar NATO a birnin Kabul na kasar Afghanistan REUTERS/Omar Sobhani
Talla

Akwai wakilan kasashen Amurka, China, Pakistan, Afghanistan da kuma Taliban da ke halartar wannan taro, a kokarin da ake na ganin cewa ‘yan kungiyar ta Taliban sun sulhunta da gwamnatin Kabul.

A makon da ya gabata gwamnatin kasar ta Afghanistan ta rataye wasu 'ya'yan kungiyar Taliban guda 6, wanda shi ne irin sa na farko tun bayan mulkin shugaba Hamed Karzai.

Taliban dai ta dage da a janye dakarun kasashen waje sama da 13,000 daga Afghanistan kafin ta amince da batun sulhu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.