Isa ga babban shafi
Faransa

Majalisar Faransa na muhawara kan kundin tsarin mulki

‘Yan majalisar kasar Faransa sun fara tafka mahawara a yau jumma'a akan bukatar nan ta yi wa kundin tsarin mulkin kasar gyara a fannin tsaro.

Firaministan Faransa Manuel Valls a lokacin da ya isa majalisar kasar domin gabatar da jawabi akan gyaran kundin tsarin mulkin kasar
Firaministan Faransa Manuel Valls a lokacin da ya isa majalisar kasar domin gabatar da jawabi akan gyaran kundin tsarin mulkin kasar REUTERS/Charles Platiau
Talla

Hakan na nufin Faransa za ta iya janye fasfo tare da tasa keyar mutum zuwa kasarsa ta asali muddun aka same sa da laifin aikata ayyukan ta’addanci

Bukatar yin gyarar dai ta biyo bayan munanan hare-haren ta’addancin da aka kai a birnin Paris a bara da suka hallaka mutane sama da 100, inda bincike ya nuna cewa ' yan ta’addan 'yan asalin kasashen ketare ne da ke da takardun zama a Faransa.

Faransa dai na ci gaba da karfafa matakan tsaro a ciki da wajen kasar don kare al’ummarta daga hare-haren kungiyoyin ‘yan ta’adda.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.