Isa ga babban shafi
Faransa

Harin Paris: Faransa da Belgium sun fadada samame

‘Yan sanda a Faransa sun kai sabbin samame a wurare 128 da ake zaton maboyan ‘yan ta’adda ne a cikin kasar, tare da sanya Jami’an tsaron dubu 115 cikin shirin ko-ta kwana bayan harin ta’addanci da ya kashe mutane 132 a birnin Paris.

Jami'an tsaro a Faransa
Jami'an tsaro a Faransa REUTERS/Yves Herman
Talla

Hukumomin Faransa da ma na Belgium sun tsaurara samame a yankunan daban-daban na kasashen su domin gano ‘yan ta’adda da ke boye a kasashen.

Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry da ke ziyara a faransa yanzu haka, ya baiyana maharan a matsayin ba ta gari tare da allawadai da lamarin

Kerry ya kuma bayyana cewa Wannan yaki ne ba wai kawai na Faransa ba, yaki ne a kan daukacin al'ummar duniya"

A halin da ake ciki dai yanzu haka ‘Yan sanda Faransa na neman Salah Abdeslam mai shekaru 26, kuma daya daga cikin mutanen da ake zargi da hannu a kai hare-haren bayan anyi amannar cewa ya tsere ta kan iyakar kasar zuwa kasarsa, Belgium.

A cewar Ministan cikin gidan Faransa, Bernard Cazeneuve, har yanzu sun gagara tan-tance mutane nawa ne ke da hannu a hari, sai dai sun yi wa mutane 100 yanzu haka daurin talala wasu 23 kuma na hannu hukuma.

Ita ma Jamus da ke taimakawa Faransa farauta masu hannu a harin kasar, a yanzu sun cafke wani mutumi guda da mata 2 a kusa da iyakar Belgium sai dai kawo yanzu ba ta tantace ko suma ‘yan ta’adda ba ne

Kazalika Britaniya ta sanar da cafke wasu maza 2 a kasarta masu shekaru 22 da 20, wanda suke tunani na da alaka da harin na birnin Paris.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.