Ukraine-Rasha
Masu sa ido na nahiyar Turai sun tsere daga kasar Ukraine bayan an yi harbi
Yau Asabar, Masu sa ido daga kungiyar hadin kai da tsaron nahiyar Turai ta OSCE, sun tsere daga Crimea na kasar Yukraine, bayan da aka ji karar harbe harbe a lokacin da suka nufi yankin. Wata majiya ta shaida wa kamfanin dillancin labarum faransa na AFP cewa, da alama anyi harbin ne a lokacin da motocin tawaggar masu sa idon ta nufi wasu shingayen da dakarun da ke goyon bayan Rasha suka sanya.Sai dai da alama ba masu sa idon aka auna da harbin ba.
Wallafawa ranar: