Isa ga babban shafi
Turkiya

Ba za a taba filin shakatawa na Gezi ba sai da amincewar kotun Turkiyya

Firayi ministan Turkiyya Racep tayyip Erdogon ya bukaci masu Zanga-zanga da su fice daga dandalin Taksim tare da daukar alkawalin cewa ba za a gudanar da aikin sake fasalta filin shakatawa na Gezi ba sai zuwa lokacin da kotu ta yanke hukunci a game da karar da masu adawa da shirin suka shigar a gabanta.

Masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Recep Tayyip Erdogan na Turkiya
Masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Recep Tayyip Erdogan na Turkiya REUTERS/Dado Ruvic
Talla

Tuni dai Erdogan ya gana da shugabannin masu zanga-zangar domin sasantawa amma wasu daga cikinsu sun ce babu wani sasantawa saboda yadda aka yi amfani da karfi wajen murkushe su.

A kalamansa na baya bayan nan, Erdogon ya ce idan dai saboda aikin sake fasalta dandanlin shakatawa na Gezi ne suke zanga-zanga, to a yau ba bu hujjar ci gaba da yin tarzoma a kasar, domin kuwa gwamnatinsa ta dakatar da shirin sai bayan kotu ta yanke hukunci a kai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.