Isa ga babban shafi
Girka

Girka na samun matsin lambar kare turbar demokradiya

Kasar Girka na samun matsin lamba daga kwamitin kungiyar Nahiyar Turai kan kare turbar demokradiya a kasar a yayin da masu ra’ayin Nazi ke kawo barazana ga kasar. Kwamishinan kungiyar kare hakkin Bil adama a Nahiyar ta Turai, Nils Muiznieks ya bayyana hakan inda ya nemi da a yi maza-maza a magance matsalar tun yanzu.  

Firaministan kasar Girka, Antonis Samaras.
Firaministan kasar Girka, Antonis Samaras. REUTERS/Yorgos Karahalis
Talla

“Matsalar ita ce idan ba a magance matsalar yanzu ba, baza a iya magance ta nan gaba ba." Inji Muiznieks.

Wadannan kalamai na Muiznieks na zuwa ne bayan wata ziyarar kwanaki biyar da ya kai a kasar ta Girka domin yunkurin dakile matsalar wariyar launin fata, wadanda rahotanni suka nuna cewa an samu akalla guda 200 da aka kawo kara a tsakanin watan Oktoban shekarar 2011 zuwa watan Disambar shekarar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.