Isa ga babban shafi
Birtaniya-IMF

Birtaniya ta yi watsi da bukatar Hukumar Lamuni

Minsitan kudin kasar Birtaniya George Osborne, ya yi watsi da wani kira da Hukumar Lamuni ta duniya IMF ta yi, inda ta nemi Birtaniya ta sassauta shirin matakan tsuke bakin aljihun da ta dauka. Kamar yadda Babban Masanin tattalin arzikin hukumar IMF, Olivier Blanchard yace tattalin arzikin kasar Birtaniya kan iya fadawa cikin wani mummunan hali.

George Osborne, Minsitan kudin kasar Birtaniya
George Osborne, Minsitan kudin kasar Birtaniya REUTERS/Toby Melville
Talla

Mista Oliviar yace yakamata kasafin kudin da Birtaniya za ta gabatar a watan Maris ya kasance a wani lokaci da za’a yi nazarin matakan da aka dauka a baya.

Sai dai Osborne ya fito ya ce, basu da shirin dakatar da matakan a yanzu, har sai sun cim ma wa’adin da aka diba, wanda zai kai har shekarar 2017 kamar yadda aka tanada.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.