Isa ga babban shafi
Birtaniya

Birtaniya na iya ficewa Kungiyar Turai idan al’ummar kasar sun amince-Cameron

Firaministan Birtaniya David Cemeron ya yi alkawalin ba al’ummar kasar damar kada kuri’ar amincewa ko ficewa daga Kungiyar Tarayyar Turai idan Jam’iyyar shi ta lashe zabe. Wannan matakin kuma ya daga hankalin Faransa da Jamus.

Firaministan Birtaniya, David Cameron a lokacin da ya ke gabatar da jawabi game da yiyuwar ficewar Birtaniya a Kungiyar Turai
Firaministan Birtaniya, David Cameron a lokacin da ya ke gabatar da jawabi game da yiyuwar ficewar Birtaniya a Kungiyar Turai Reuters/Suzanne Plunkett
Talla

Sai dai Cameron yace zai yi kokarin sasanta huldar Bitaniya da kungiyar Turai kafin ya ba Al’ummar kasar damar kada kuri’a.

Mista Cameron yana nufin Birtaniya za ta fice daga kungiyar Tarayyar turai idan Al’ummar kasar sun amince ko kuma idan sun amince a koma teburin sasantawa.

Sai dai akwai gargadi da Faransa da Jamus suka gabatar wa Birtaniya game da wannan kudirin  Yanzu haka kuma David Cemeron ya fara fuskantar suka daga Jam’iyyar adawa ta Labour wadanda suka ce alamun gazawa ne ga Firaministan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.