Girka
Ma’aikata sun shiga yajin aiki a Girka
A Yau ma’aikata a kasar Girka za su sake gudanar da wani yajin aikin gama gari, saboda shirin gwamnatin kasar na ci gaba da daukar matakan tsuke bakin aljihu, wanda zai bai wa kasar damar samun Karin tallafi. Yajin aikin yau ya kasance na 20, tun bayan barkewar matsalar tattalin arzikin da ya abkawa kasar shekaru biyu da suka gabata. Sau da yawa zanga zangar adawa da matakan tsuke bakin aljihu kan rikede ta koma rikici.
Wallafawa ranar: