Isa ga babban shafi
Girka

Yunkurin kafa gwamnatin hadin gwiwa a Girka ya gamu da cikas

Yunkurin kafa gwamnatin hadin gwiwa a kasar Girka ya gamu da cikas bayan Jam’iyyar Syriza ta yi barazanar hada kai da sauran jam’iyyun siyasar kasar. A Yau Litinin ne aka yi hasashen shugaban kasa, Carolos Papoulias, zai jagoanci manyan Jam’iyun kasar uku, don cim ma yarjejeniyar kafa gwamnatin hadin kai.

Alexis Tsipras, Shugaban Jan'iyyar  Syriza,  a lokacin da yake ganawa da magoya bayan shi bayan kammala zabe
Alexis Tsipras, Shugaban Jan'iyyar Syriza, a lokacin da yake ganawa da magoya bayan shi bayan kammala zabe Reuters/Eurokinissi
Talla

Tun a zaben ranar 6 ga watan Mayu ne masu kada kuri’a suka yi watsi da jam’iyyun da ke goyon bayan matakan tsuke bakin aljihun gwamnati da  kungiyar kasashen Turai da hukumar Bada Lamuni ta IMF ke bukata.

Idan dai har Jam’iyyun suka kasa cim ma samar da gwamnatin hadin gwiwa, ya dole a sake gudanar da zabe a watan Yuni.

Sauran Jam’iyyun Siyasar kasar dai suna ganin samar da gwamnati ba tare da samun goyon bayan Jam’iyyar Syriza cikas ne saboda yunkurin samun goyon bayan Majalisa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.