Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Naja’atu Muhammad kan hukuncin zabe a Najeriya

Wallafawa ranar:

‘Yan Najeriya na ci gaba da bayyana damuwa a kan yadda kotuna ke karbe hurumin da kundin tsarin mulki ya bai wa Hukumar zabe na bayyana wadanda suka samu nasarar zabubbukan da jama’a suka yi, wajen bayyana wasu daban a matsayin halartattun wadanda suka yi nasara. 

Hajiya Naja'atu Bala Muhammad tsohuwar kwamishiniya a Hukumar kula da ayyukan 'yan Sandan Najeriya.
Hajiya Naja'atu Bala Muhammad tsohuwar kwamishiniya a Hukumar kula da ayyukan 'yan Sandan Najeriya. © Daily Trust
Talla

Wannan ya biyo bayan yadda kotunan suka sauya sunayen wadanda hukumar zabe ta sanar sun samu nasara a zabbubukan gwamnoni da kuma ‘yan majalisun kasar. 

Ko a wannan mako, kotuna sun soke zabubbukan gwamnonin Zamfara da Kano, yayin suka tabbatar da na jihohin Lagos da Bauchi. 

Dangane da wannan korafi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Naja’atu Muhammad, ‘yar siyasa, kuma mai sharhi akan harkokin Najeriya.

Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.