Bakonmu a Yau
Tattaunawa da PFS Saminu Yusuf Abdullahi kan rushewar gini a Kano
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:41
Har zuwa cikin daren jiya talata an ci gaba da kokari domin ceto tarin mutanen da da wani gini ya rufta a kansu, lokacin da su ke tsaka da hada-hadar kasuwanci a kasuwar Beirut da ke jihar Kano a Najeriya, duk da ya ke wasu sun yi korafi dangane da yadda aka fara gudanar da ayyukan ceton a makare. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Mai magana da yawun hukumar kwana-kwana a jihar ta Kano wato PFS Saminu Yusuf Abdullahi.