Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Farfesa Shehu Abdullahi Zuru kan nasarar William Ruto a zaben Kenya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:41
Shugaban hukumar zaben Kenya Wafula Chebukati ya bayyana cewar mataimakin shugaban kasa William Ruto ne ya lashe zaben shugaban kasa na ranar 9 ga watan Agusta, saboda samun kuri’u sama da miliyan 7, fiye da na Raila Odinga wanda ya samu kasa da miliyan 7.Sai dai kafin gabatar da sakamakon, 4 daga cikin kwamishinonin zabe 7 sun ki amincewa da sakamakon. Kan haka Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami’ar Abuja, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.