Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

IMF ya sake kira ga Najeriya kan neman soke tallafin man fetur

Wallafawa ranar:

Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya sake kira ga gwamnatin Najeriya da ta soke tallafin man fetur da kuma farashin canjin kudade a hukumance, tare da daukar matakan rage radadin da hakan zai haifarwa marasa karfi.

Shugabar asusun ba da lamuni na duniya IMF, Kristalina Georgieva.
Shugabar asusun ba da lamuni na duniya IMF, Kristalina Georgieva. REUTERS - POOL
Talla

A ranar 24 ga watan Janairun da ya gabata ne dai gwamnatin Najeriya ta bayyana dage shirinta na cire tallafin man fetur a bana, matakin da IMF ya ce ba zai dore ba.

Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Kasim Kurfi masanin tattalin arziki da ke Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.