Isa ga babban shafi

Sojojin Nijar sun yi barazanar kashe Bazoum idan aka kai musu farmaki

Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar sun yi barazanar kashe hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum idan har kasashen makwabta suka yi yunkurin amfani da karfin Soji don dawo da shi kan karagar mulki.

Jagoran mulkin Sojin Nijar Janar Abdourahamane Tiani a gefe kuma hambararren shugaban kasar Bazoum Mohamed.
Jagoran mulkin Sojin Nijar Janar Abdourahamane Tiani a gefe kuma hambararren shugaban kasar Bazoum Mohamed. © AP / AP - Ludovic Marin / Montage RFI
Talla

Wasu manyan jami’an kasashen yamma 2 sun tabbatar da matsayar sojojin na Nijar ga kamfanin dillancin labarai na AP.

A cewar majiyoyin, Sojojin sun shaidawa karamar sakatariyar wajen Amurka Victoria Nuland a ziyarar da ta kai Nijar cikin makon nan cewa tabbas za su kashe Bazoum idan har wata kasa ta tasamma kai musu hari.

Kamfanin na AP ya ruwaito cewa hatta guda cikin jami’an Amurka ya tabbatar da wannan batu.

Bazoum wanda sojoji suka hambarar da gwamnatinsa a ranar 26 ga watan jiya, ya bayyana cewa ana ci gaba da tsare shi a cikin gidansa da ke fadar shugaban kasa, inda koka da nau’in abincin da Sojojin ke ciyar da shi.

Wannan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da kungiyar ECOWAS ta umarci dakarunta su kasance cikin shirin kai hari kasar ta Nijar don tabbatar da dawowar mulkin Demokradiyya a kasar ta yammacin Afrika.

Yayin taron shugabannin kasashen kungiyar da ya gudana a Abuja jiya Alhamis, dukkaninsu su tafi akan matsayin matsa lamba ga sojojin na Nijar don tabbatar da dawowar mulkin farar hula.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.