Nijar-Agadez
Karancin ruwa da bayyanar kwari a gonaki na barazana ga manoman Agadez
Manoma a jihar Agadas da ke arewacin jamhuriya Nijar sun samu kan su a halin tsaka mai wuya sakamakon matsalar karancin ruwan sama da aka samu a bana baya ga bullar kwarukan fari wadanda ke lallata amfanin gona a wasu yankunan jihar. Masana na kashedin yadda wannan lamarin ka iya haifar da karancin abinci da hauhawar farashi a kasuwanni, sai dai gwamnati ta ce ta na daukar matakai domin magance lamarin. Daga Agadez ga rahoton wakilinmu, Umaru Sani.
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:01