Isa ga babban shafi
Nijar

'Yan bindiga sun tarwatsa 'yan gudun hijira a Nijar

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa dubban mutane ne suka tsere daga sansanin ‘yan gudun hijira da ke Intikane a cikin jihar Tawa gab da iyakar kasar da Mali, bayan da ‘yan bindiga suka kai hari tare da kashe mutane a kalla 3 a ranar Lahadin da ta gabata.

Wasu daga cikin 'yan gudun hijira
Wasu daga cikin 'yan gudun hijira REUTERS/Luc Gnago
Talla

Ofishin Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira na Majalisar Dinkin Duniya da ke Nijar ya ce, yanzu mutane dubu uku da suka tsere sun samu mafaka a garin Tlemces mai tazarar kilomita 27 daga sansaninsu na farko.

A kalla dai ‘yan asalin kasar Mali dubu 20 ne ke rayuwa a sansanin da aka kai wa harin, tare da wasu dubbai ‘yan Nijar da suka guje wa tashe-taashen hankulan da ake fama da su

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.