Isa ga babban shafi
Nijar

Mayakan Boko Haram sun kashe mutane 5 a Tumur dake Diffa a Nijar.

Rahotanni daga kauyen Tumur dake kusa da Bosso a jihar Diffa na kasar Janhuriyar Nijar na cewa ‘yan kungiyar Boko Haram sun kai wani kazamin hari inda suka kashe mutane biyar da kona gidaje shida 

Shugaba Issoufou Mahamadou a lokacin da yake rantsuwar kama aiki ranar  2 Aprilu 2016 a  Niamey.
Shugaba Issoufou Mahamadou a lokacin da yake rantsuwar kama aiki ranar 2 Aprilu 2016 a Niamey. BOUREIMA HAMA / AFP
Talla

Majiyoyin samun labarai na cewa yammacin jiya Juma'a aka kai wannan hari duk da cewa jami'an tsaro na iyakacin kokarin kawo karshen ayyukan hashsha da ‘yan kungiyar ke yi a yankunan.

Yanzu haka dai jami'an tsaro daga kasashen Najeriya, Nijar, Kamaru da Chadi na iyakacin kokari ne domin kakkabe guggubin ‘yan kungiyar Boko Haram da suke hana sukuni a kauyukan dake kan iyakokin kasashen yankin.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.