Isa ga babban shafi

Mutane sun mutu sakamakon ruftawar rami a Zamfara

Akalla mutane biyu ne suka mutu sannan wasu 10 suka jikkata a ranar Larabar da ta gabata sakamakon ruftawar wata mahakar zinari a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya, kamar yadda wani jami'in hukumar kula da agajin gaggawa ta kasar ya sanar.

Injinin nikan dutsi a wajen aikin sarrafa tace zinari a garin Bagega Jahar Zamfara
Injinin nikan dutsi a wajen aikin sarrafa tace zinari a garin Bagega Jahar Zamfara RFI/Awwal Janyau
Talla

An gano gawarwakin mutanen  biyu sannan mutane 10 na da raunuka daban-daban.

Babu wani bayani dangane da  adadin masu hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba da ake zaton sun mutu a wannan wuri biyo vayan wannan iftila’in ko suka makale a karkashin kasa," in ji Aliyu Kafindangi, manajan horar da jami’an hukumar kula da agajin gaggawa ta kasar Nema a arewa maso yammacin Najeriya.

A cewarsa, an ci gaba da aikin ceto a yau Asabar a kauyen Dan Kamfan, domin fito da gawarwakin masu hakar ma’adinai da suka makale a hadarin.

Wani filin hakar ma'adanai a jihar Zamfara da ke Najeriya.
Wani filin hakar ma'adanai a jihar Zamfara da ke Najeriya. © REUTERS/Afolabi Sotunde

Kawo yanzu dai ba a san dalilan ruftawar wannan rami ,sai dai ana yawan samun hadurra a mahakar ma'adanai a yankin, gani ta yada mutane ke aiki ba bisa ka’ida ba  kuma hanyoyin da ake amfani da sun bambanta da na zamani.

A bisa wasu dalilai na tsaro gwamnatin jihar Zamfara ta sake haramta ayyukan hakar ma'adanai a watan Satumban 2023. Jihar Zamfara na daya daga cikin yankunan kasar da ke fama da matsaloli da suka jibanci  rashin tsaro .

Jami'an tsaro na sintiri yayin da mutane ke jiran isowar 'yan matan makarantar da aka ceto a Jangebe, da ke jihar Zamfara a Najeriya. 3 ga watan Maris, 2021.
Jami'an tsaro na sintiri yayin da mutane ke jiran isowar 'yan matan makarantar da aka ceto a Jangebe, da ke jihar Zamfara a Najeriya. 3 ga watan Maris, 2021. © REUTERS/Afolabi Sotunde/File Photo

A cikin 'yan shekarun nan a Najeriya, ayyukan hakar ma'adinai na janyo hadura ,al’amarin da ya as hukumomin sanar da daukar matakan sa ido a wannan sashe duk da cewa ana kyautata zaton kungiyoyi masu dauke da makamai na amfani da haka a wasu lokuta don afkawa ma’aikata  da nufin yi musu fashi da makami.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.