Isa ga babban shafi
Rahoto

MDD za ta inganta kiwon lafiya a jihar Yobe ta Najeriya

Majalisar Dinkin Duniya ta yi alkawarin tallafa wa harkokin kula da lafiya a jihar Yobe ta Najeriya wanda ake sa ran zai  samar da ingantaciyar lafiya ga mutane miliyan uku a jihar, yawancinsu wadanda matsalar ta Boko Haram ta shafa.

Wani kwararren likita a Najeriya Japhet Udokwu, yayin duba lafiyar wasu kananan yara a garin Damaturu dake jihar Yobe.
Wani kwararren likita a Najeriya Japhet Udokwu, yayin duba lafiyar wasu kananan yara a garin Damaturu dake jihar Yobe. REUTERS - SEUN SANNI
Talla

Matsalar tsaro ta yi matukar illa ga bangaren kiwon lafiya a jihar ta Yobe, inda ya sa gwamnatin tare da Majalisar Dinkin Duniya suka kudiri aniyar farfado da bangaren na kiwon lafiya don saukaka wa al'umma wahalar da suke sha a yanzu.

Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken rahoton Bilyaminu Yusuf 

Majalisar Dinkin Duniyar ta yaba wa gwamnatin jihar ta Yobe kan yadda ta samar da wasu cibiyoyi na kula da lafiyar kananan yara da mata da ke rasa rayukansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.