Tallafin Uwargidan shugaban Najeriya ya bar baya da kura a Filato
Fulani makiyaya a jihar Filato da ke Najeriya sun koka a bisa kokarin mayar da su saniyar ware da suka ce gwamnati na yi kan amfana da tallafin naira miliyan 500 da Uwargidan shugaban Najeriya, Sanata Remi Tinubu, ta bayar, don rabawa iyalai 500, wadanda rikicin watannin baya bayan nan da ya barke a sassan jihar ya rutsa da su.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:37
Talla
Iyalan da za su amfana da tallafin dai za su karbi naira miliyan guda-guda ne kowannensu a kananan hukumomi shida da suka hada da Bassa, Barkin Ladi, Bokkos, Jos ta Kudu, Mangu da Riyom.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu