Mutane 20 sun makale a cikin wani bene da ya rushe a Abuja
Rahotanni daga Najeriya na cewa wani gini mai hawa hudu ya rushe a yankin Life camp da ke birnin tarayyar kasar Abuja.
Wallafawa ranar:
Ganau sun shaidawa manema labarai cewa ginin wanda ake kan aikin sa yanzu haka ya fado ne da yammacin jiya Litini, kuma ana fargabar ya danne mutane fiye da 20.
Kafofin yada labaran cikin gidan kasar sun ruwaito cewa dama inda ake ginin ya gamu da ibtila’in ambaliyar ruwa a makon da ya gaba, amma bayan janyewar Ruwan ma’aikatan suka koma don ci gaba da aiki.
Tun lokacin faruwar lamarin ne kuma jami’an hukumar bada agajin gaggawa da na kashe gobara suka isa wajen don kokarin zakulo mutanen da suka makale a karkashin baraguzan ginin da ya fado.
A cewar jaridar Leadership da ake wallafawa a kasar, karfe 8 saura na daren litinin din an samu nasarar ceto mutane 9.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu