Buhari ya sanyawa tashoshin jiragen sama sunan fitattun ‘yan kasar
Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sanyawa tashoshin jiragen saman kasar mallakar gwamnatin tarayya sunayen wasu fitattun jama’ar kasar da suka bada gudumawa a fannoni daban daban.
Wallafawa ranar:
Sanarwar da kakakin ma’aikatar sufurin jiragen sama Odutayo Oluyesi ya rabawa manema labarai, ta bayyana cewa Buhari ya amince da sanya sunayen ne a ranar juma’ar da ta gabata.
Daga cikin wadanda aka nada sunayen su akwai Sheikh Usman Danfodio da Obafemi Awolowo da janar hassan Usman Katsina da Janar Tunde Idiagbon da JS Tarka.
Wasu daga cikin tashoshin da nadin sunan ya shafa sun hada da na Akure da Dutse da Binin da Gombe da Maiduguri da Yola da Akure da kuma Kaduna.
Ga jerin tashoshin da kuma sunayen da aka rada musu.
Ibadan – Samuel Ladoke Akintola
Ilorin – Janar Tunde Abdullahi Idiagbon
Kaduna – Janar Hassan Usman Katsina
Maiduguri – Muhammadu Buhari
Makurdi – Joseph Sarwuan Tarka
Minna – Abubakar Imam
Nasarawa – Sheikh Usman Danfodio
Asuba – Alfred Diete Spiff
Fatakwal – Obafemi Jeremiah Awolowo
Yola – Lamido Aliyu Mustapha
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu