Maniyyatan farko a Najeriya sun yi hatsari a kan hanyar su ta zuwa filin jirgi
Wata mota dauke da maniyyata daga jihar Nassarawa sun yi hatsari, yayin da ssuke kan hanyar su ta zuwa filin jirgin saman Abuja babban birnin kasar, domin zuwa kasa mai tsarki.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Motar mai daukar mutum 18 ta yi hatsarin ne a daidai kauyen Kara, da ke yankin karamar hukumar Keffi.
Rahotanni basu bayyana cewa ko an samu asarar rai ba, amma wasu daga cikin maniyyatan sun samu rauni.
Jihar Nassarawa ce za a fara diban maniyyatan farko a Najeriya, inda za su tashi daga Abuja.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu