Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa a Kwara
Dan takarar kujerar shugabancin Najeriya na jam’iyyar APC, Asiwaju Ahmed Bola Tinubu ya lashe mafi rinjayen kuri’un da aka kada a zaben shugaban kasar da ya gudana a jihar Kwara.
Wallafawa ranar:
Sakamakon da hukumar zaben Najeriya INEC ta sanar, ya nuna cewar daga cikin kuri’un da aka kada, Sanata Tinubu ya samu kuri’u 263,572, yayin da dan takarar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya samu kuri’u 136,909.
Dan takarar jam’iyyar Labour Party LP, Peter Obi ne ya zo na uku, bayan samun kuri’u 31,166.
Ana sa ran mika sakamakon zaben zuwa cibiyar hedikwatar hukumar INEC da ke Abuja.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu