Isa ga babban shafi

Najeriya: Zamfara ta bai wa dan bindiga sarauta don samun zaman lafiya

 A Najeriya, masarautar ‘Yan Doton Daji  dake jihar Zamfara a arewa maso yammacin kasar ta nada wa wani kasurgumin dan bindigan nan da ake kira Ada Aliero sarautar Sarkin Fulanin Yandoto.

Ada Aleiro, kasurgumin dan bindigan da aka bai wa sarautar gargajiya a Zamfara.
Ada Aleiro, kasurgumin dan bindigan da aka bai wa sarautar gargajiya a Zamfara. © Aminiya - Daily Trust
Talla

An gudanar da bikin nadin ne duk kuwa da cewa an sanar da dakatar da shi tun da farko bisa wani sako da aka samu daga hukumomin jihar, kamar yadda jaridar ‘Daily Trust’ da ake wallafawa a Najeriya ta ruwaito.

Sai dai duk da haka bikin ya samu halartar shugaban karamar hukumar Tsafe  da kwamishinan tsaro na jijhar Zamfara, Ibrahim Mamman Tsafe.

Wasu majiyoyi sun ce an yanke shawarar yi wa Aleiro wannan sarautar ce  sakamakon rawar da ya taka wajen cimma yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin masauratar da ‘yan bindiga  da ke addabar karamar hukumar Tsafe.

Majiyoyi daga fadar kuwa sun ce gwamnatin jihar ta yi umurnin dakatar da nadin ne bisa fargabar yadda al’umma za su dauki lamarin, bayan da wasu kafafen yada labarai suka bankado shirin.

Sai dai shugaban kwamitin kwance damarar 'yan bindiga a jihar Zamfara ya tabbatar wa da sashen Hausa na RFI cewa lallai an yi wannan nadi ne don a samu zaman lafiya mai dorewa a jihar, duba da cewa babu wani zabi da ya wuce haka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.