Isa ga babban shafi

Gwamnan Sokoto ya janye dokar hana fita ta sa'o'i 24

Gwamna Aminu Waziri Tambuwal ya janye dokar hana fita da ya kafa a cikin birnin Sokoto, matakin da ya ce ya fara aiki nan take, inda ya kuma haramta duk wani nau'i na gangami, ko jerin gwano a jihar har sai abinda hali yayi.

Harabar Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari, inda fusatattun dalibai suka kashe wata daliba mai suna Deborah Emmanuel saboda yin batanci ga Annabi Muhmmad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi.
Harabar Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari, inda fusatattun dalibai suka kashe wata daliba mai suna Deborah Emmanuel saboda yin batanci ga Annabi Muhmmad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi. AP - Olu Akinrele
Talla

Gwamnan ya ce matakin ya biyo bayan tuntubar juna da hukumomin tsaro da abin ya shafa.

An dai kafa dokar hana fita ta sa'o'i 24 a birnin Sokoto ne bayan wata zanga-zanga da ta yi sanadin mutuwar mutum daya a jihar, kamar yadda wakilinmu ya tabbatar, yayin da wasu da dama suka jikkata a yayin zanga-zangar da ta janyo kafa dokar hana fitar a birnin Sokoto da kewayensa.

Masu zanga-zangar sun nemi sakin mutane biyu da ake zargi da kashe Deborah Samuel, bisa tuhumarta da batanci ga Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi.nura

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.