'Yan bindiga sun kashe sama da mutane 50 a Zamfara
Akalla mutane 56 suka mutu a jihar Zamfara dake Najeriya, sakamakon wani hari da ‘yan biondiga suka kai wasu kauyuka uku a karamar hukumar Bakura ta jihar.
Wallafawa ranar:
Wani tsohon kansilan da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Jaridar Premium Times ‘yan bindigar sun kai hari a Sabon Garin Damri, na kauyukan da misalin karfe 2:30 na ranar Jumma’a.
Ya ce ‘yan bindigar sun kai hare-haren ne da ake ganin kamar na bai daya a Sabon Garin Damri da Damri da Kalahe kafin rundunar hadin gwiwa ta jami’an tsaro su tunkare su.
Wani mazaunin garin Mu’azu Damri ya ce da adadin wadanda suka mutu zai fi haka idan jami’an tsaro ba su tunkari ‘yan bindigar ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu