Mazauna yankunan Zamfara na ci gaba da barin gidajensu saboda 'yan bindiga
Daruruwan mazauna kauyukan Magazu da Marke, a karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara a arewa maso gabashin Najeriya ne suka tsere daga gidajensu sakamakon yadda ‘yan ta’adda da aka fi sani da ‘yan bindiga suka zafafa kai musu hare hare.
Wallafawa ranar:
Mazauna yankuna sun ce Magazu, wanda shine mazaba mafi girma a karamar hukumar Tsafe, ya kasance kusan babu kowa a halin da ake ciki.
Jaridar Premium Times da ake wallafawa a Najeriya ta ruwaito wasu majiyoyi na cewa al’ummomin wadannan yankunan sun gaji da hare hare da ake kai musu ba kakkautawa, lamarin da ya sa suka fara barin gidajensu tun daga yammacin Alhamis.
Hare haren ‘yan bindiga sun fi yin kamari a karamar hukumar Tsafe idan aka kwatanta da saura yankunan jihar Zamfara, wadda rashin tsaro ya yi mata dabaibayi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu